ibnhujjah
002 HUKUNCE – HUKUNCEN JANAZA A SAWQAQE
TAKARDA TA FARKO {1}
WANKA DA ABUBUWAN DA KE DA ALAQA DA SHI
DARASI NA BIYU {2}
GABATARWA:
Dukkan yabo da jinjina sun tabbata ga Allah, tsira da amincinSa su kara tabbata ga annabinSa (S.A.W).
Bayan hak, wannan wani dan takaitaccen runutune da na yi tare da umarnin malamina Mal. Basheer Lawal Muhammad Zaria. Domin karantar da mutanen Masallaacinmu {Masjidul Imam Muhammad Ibn Abdilwahab}.wanda ke layin Zamfara Tudun Jukun Zaria Kaduna, Nigeria.
Allah na ke roko ya bani ikon rubuta abin da yake daidai kuma ya amfanar da ni da ku baki daya yasa mu cika da Imani
ME AKE MA MUTUM DA ZARAR YA RASU?
Da zarar dan uwanka/ki ya rasu ana so a yi ma sa wadannan abubuwan masu zuwa.
Rufe masa idanuwansa kamar yadda manzon Allah {S.A.W} ya yi wa Abi Salmah.
Yi masa addu’a.
Rufe masa gaba daya jikinsa kamar yadda Nana Aisha ta fada cewa haka aka yi wa Manzon Allah {S.A.W} da ya rasu aka rufe gaba daya jikinsa.
Gaggawar shirya shi a yi masa wanka da yi masa likkafani.
Cire masa kayan jikinsa da gaggawa.
A yi saurin zartar da wasiyyarsa.
Gaggawar biya ma sa bashi.
Rubutawar:
Yusuf Lawal Yusuf
(Abu Ja’@far)