ibnhujjah
JAGORAN MATAFIYA
Fitowa ta biyu
Wallafar : Sheik Dr. Abdullahi Sale Pakistan Kano
( Ladabi Na Biyu ) 2
Matafiyi Ya Nemi Yardar Allah
Ya zama wajibi ga mai aikin Hajji ko Umara ya yi nufin neman yardar Allah ga aikin Hajjinsa ko Umararsa kuma ya yi taka-tsantsan, kada ya nufi al’faharin duniya ko fariya ko riya ko don ace masa Alhaji, domin yin haka yana sabbaba lalacewar aiki da rashin karbuwarsa.Allah madaukakin sarki ya ce: “kace lallai sallata da yankata da rayuwata da mutuwata ga Allah Ubangijin halittu Suke Shi kadai babu abokin tarayya a gare shi da haka aka umarce ni kuma nine farkon mai mika wuya gare shi.” Suratul An’am: 162-163
Kuma Allah madaukakin Sarki ya ce: “Ka ce ni mutum ne tamkarku, sai dai ana yimin wahayi a gareni, cewa Ubangijinku abin bautarku, Ubangiji ne guda daya, duk wanda ya kasance yana kaunar haduwa da Ubangijinsa, ya yi aiki na kwarai, kada yayi shirka da a bautawa Ubangijinsa tare da wani.” Al’kaffi 110.
Kuma Allah madaukakin Sarki ya ce: “Wanda ya kasance yana nufin magaggauciya ( Duniya ) zamu gaggauta ba da abin da mukaga dama ga wanda mukaga dama, sannan mu sanya wutar jahannama makoma gare shi, ya shige ta yana abin zargi kuma yana kaskantacce .” Isa’i: 18.
Kuma yazo a cikin Hadisin kudusi ; Allah ya ce: “Ni ne mafi wadatuwa daga shirkar masu shirka, wanda duk ya aikata wani aiki yayi shirka a cikinsa, to, zan bar shi da shirkarsa.” Musulimu ne ya ruwaito shi a cikin littafin Zuhudu, Babin wanda ya yi shirka da Allah a ciki aikinsa, lamba : 2985
Muhadu a fitowa ta gaba ……………
DAGA ABDULLAHI NAGEGIME