ibnhujjah
BABU ZAKKA A DUKIYAR WAKAFI ! ! Tambaya:
Malam ya halatta idan aka gina masallacin Jumu'a sannan aka gina shaguna ajikinsa domin su dinga kawo masa kudin gudanar da shi, to malam idan kudin yakai nisabi za'a iya fitar musu da zakkah? Allah ya kara basira ameen. Amsa: To dan'uwa duk dukiyar da babu wani ayyanannen mutum da ya mallake ta babu zakka a cikinta, don haka babu zakka a wakafi, ko dukiyar da mutane suka hada saboda taimakekeniya, in wata matsala ta samu wani daga cikinsu kamar hadari. ko da kuwa ana juya kudin suna kawo riba, shagunan masallaci wakafi ne, don haka ba za'a fitar musu da zakka ba. Don neman karin bayani duba Fataawa Allajnah Adda'imah : 91. Allah ne mafi sani. Jamilu Zarewa