ibnhujjah
Tambayata 013* *Mace ce ta tafi yaji (suka bata damijin amma ba sakiba), tana gida kafun asasanta tadawo gidan mijinta sai Allah ya karbi rayuwar mijin nata, sai tadawo gidan mijinta zatayi takaba sai uban mijin yace takoma gidansu tayi takabar. To menene abun yi?* *Amsa* A hakikanin gaskiya , idan mace mijinta yamutu inda shariah ta tabbatar tayi takaba shine d'akin mijinta. Sawa'un gidansa ne ko gidan haya, koda gidan hayane anan ne zata zauna tayi takaban, yakamata mai gidan ya tausaya mata saboda halin da take ciki, inko yaki saboda ba tausayi sai wasu daga cikin 'yan uwa musulmi, kamar danginsa su biya mata. Don k'a idar takaba shine ta zauna adakin mijinta don shine yake dai dai da nassi. Abunda uban yayi bai kyauta ba yakamata yayi hakuri yabarta tayi takaba ad'akin mijinta don shine yafi dacewa shariah. Sannan zaman takaba mace zata zauna ne bazata fitaba inba laluraba, bazatayi adoba, bazata sa kaya me tsada ba, bazata sa kwalli ba, bazatayi wanka ko wanki da sabulu mai kamshiba, bazatayi kitsoba , (in miji ta yarasu da kitso akanta bazata tsefeba har wata hudu da kwana goma) bazatayi lalle ba, bazata je makaranta taji darasi ta dawoba. Sannan da zaran taji mijinta ya rasu zata shiga takaba ba sai tajira wata tsofuwa ta shigar da itaba, in da kaya me kyau ajikinta sai tacire, inda jambaki abakinta sai wanke. Kuma haka da zaran tayi wata hudu da kwana goma shikenan tafita atakaba ba sai tajira wata taxo tafitar da itaba. *Wannan tambaya yana daga cikin amsoshin da
Sheik Jafar ya amsa alokacin rayuwarsa.Allah Ya gafartawa Malam Yakarbi Shahadarsa.