ibnhujjah
INA CIKIN IDDA, SAI WANI YA YI ZINA DA NI !
YAYA ZAN YI ?
Tambaya :
Malam mijina ya sake ni, bayan na yi tsarki
daya, sai rikici ya kaure tsakanin arna da
musulmai a garinmu, sai wani crister, ya
dauke ni ya yi zina da ni, yanzu malam yaya
zan yi game da idda ta ?
Amsa :
To 'yar'uwa ina rokon Allah ya kawowa
musulmi dauki a Nigeria, wannan mas'alar ta
ki malamai sun yi sabani akanta, akwai
malaman da suka tafi akan dole sai kin yi
istibra'i bayan kin gama idda, saidai maganar
da tafi zama daidai ita ce : kawai za ki karasa
iddarki ne, ba sai kin yi istibra'i ba bayan kin
kammala, saboda babbar manufar istibra'i ita
ce kubutar mahaifa, hakan kuma zai tabbata
idan kika karasa jinane biyun da suka rage
miki na iddarki.
Yana daga cikin saukin addinin musulunci
kasancewar duk ibadojin da za su iya shiga
cikin juna kuma manufarsu daya ce, jinsinsu
guda ne, to daya za ta shiga cikin daya,
kamar wacce ta yi jima'i sai kuma haila ta zo
mata, wanka guda daya ya ishe ta a karshen
hailarta.
Allah ne mafi sani.
Duba : Majmu'ul fawa'id na Sa'ady shafi na :
141.
Jamilu Zarewa