ibnhujjah
JAHILAN ‘YAN JARIDUNMU SUNA DORA
AL’UMMARMU A KAN JAHILCI:
1. Abin bakin ciki, da takaici, jahilan ‘yan
jaridunmu, musamman ma masu aiki a
manyan gidajen rediyo na duniya; kamar BBC,
VOA, RFI, DW-radio, da sauransu su ne suke
kara cusa al’ummar hausawanmu cikin
jahilci, da rikici a cikin wasu mas’aloli da
suka jibinci Shari’ah.
2. Misali mu a nan Nigeria a yau talatan nan
muna yinin 27 ne ga Ramadan, shi kuwa
daren 27 tuni ya riga ya wuce, to amma
saboda abin da wadannan ‘yan jaridu suke
yadawa a kullum sai ga shi mutane da yawa
sun dauka cewa sai can anjima ne daren 27 ga
Ramada zai shigo, a inda za su kara kaimi
cikin ibada domin dacewa da daren lailatul
kadri, alhalin su ba su sani ba wannan dare
na 27 tuni ya riga ya wuce.
3. Yana da kyau Al’ummah su san cewa a bisa
ka’idar tsarin lokaci dare shi ne farko, sannan
yini ya biyo baya, to amma abin bakin ciki
jahilan ‘yan jaridunmu sun toge a kan akkasa
wannan hakika ga al’ummar hausawanmu.
Allah Ka fahimtar da wannan Al’ummah
tamu. Ameen.