ibnhujjah
*MIJINA BA YA AZUMI SAI YA GA WATA, KO YA HALATTA NA BUTSARE MASA ???*
*Tambaya*
Salamun alaikum, Dr.
Tambaya ce aka jefa mani ina gabatar da darasi wa mata, mace ce mijinta bai yarda ya dauki azumi ba sai ya ga wata da kansa )bai yarda da sanarwar Sarkin Musulmi ba(, to inda mushkilar take shi ne, ita matarsa ta yarda da sanarwar Sarkin Musulmi amma sai ya ce kada ta kuskura ta dauki azumin, to shin minene matsayinta? Domin ta ajiye azumin saboda tsoron kada ya wulaqanta ta.
*Amsa*
Wa alaikum assalam A Zahiri ba za ta masa biyayya a nan ba, Tun da Azumi rukuni ne daga cikin ginshikan musulunci.
Annabi SAW yana cewa:
""
"Ana yiwa jagora biyayya ne idan ya yi umarni da abin da ya dace da sharia"
Sannan yana cewa: "Ana yin azumi ne ranar da mutane suke yin azumi"
Allah ne mafi sani
*Amsawa*
*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*