ibnhujjah
_TA KI YARDA DA MIJINTA SABODA TANA AZUMIN NAFILA??_*
*_Tambaya_*
AssalamuAlaikum.
Mallam inna da tambaya ? Yaya hukuncin Matar da miji ya bukacheta sannan tana Azumin sunna. Ta ki ta Aminche mishi
*_Amsa_*
Wa aleikum assalam,
ta yi kuskure ya kamata ta amsa kiran mijinta, saboda azumin sunna ya halatta a karya shi ko da babu dalili, Annabi (SAW) yana cewa"Mai azumin nafila sarkin kansa ne ina ya Ga dama ya cigaba da azumin, in kuma ya so ya karya " kamar yadda Tirmizi ya rawaito a Sunan
Allah ne mafi sani.
*_Dr, Jamilu Zarewa_*