ibnhujjah
*YA YAGA TAKARDAR SAKIN KAFIN MATARSA TA GANI?*
*Tambaya
ASSALAMU ALAIKUM. MALAM SHIN IDAN MUTUM YA RUBUTA TAKARDAR SAKI YA AJE, SAI WANI YA GANI SHIN MATAR TA SHI TASAKU?
*Amsa:*
Wa alaikum assalam To malam matukar ya rubuta da niyya kuma yana cikin hayyacinsa ba takura masa aka yi ba, to ta saku, saboda fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : "Allah ya yafewa al'umata abin da ta riya a zuciyarta, mutukar bata fada ba, ko ta aikata" ka ga kuma rubutu aiki ne.
Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana zartar da abubuwa da yawa ta hanyar rubutu, ka ga ya zama hujja kenan.
Wannan shi ne mazahar Abu-hanifa da Malik kuma shi ne zancen Shafi'i mafi inganci. Duba Al-mugni : 76
Allah ne mafi sani
*Amsawa*✍
*DR. JAMILU YUSUF ZAREWA*