ibnhujjah
ZAN IYA AURAN ‘YAR KANWAR MATATA?*
*Tambaya:?*
Assalamu alaikum
Malam, Ya halatta mutum ya auri yar qanwar matarsa?
*Amsa:*
Wa alaiku assalam,
Ya halatta ya aure ta, bayan ya saki matarsa, amma bai halatta ya hada su ba saboda innarta ce. Annabi(S.A.W.)yana cewa: “Ba’a a hada mace da goggonta, ba’a hada mace da innarta a auratayya, saboda in kuka yi haka, za ku lallata zumunci ku” kamar yadda ibnu Hibban ya rawaito.
Allah ne mafi sani
*Amsawa*
*Dr.Jamilu Yusuf Zarew*