Sulaiman Muhammad
ibnhujjah Assalamualaikum warahatullah wabarkatahu,
Tambayana anan shine, malam minene isnadi na wannan hadisin
KU KIYAYI ZINA
A’amash ya ruwaito daga Sufyan daga Huzaifah bn Alyaman (ra) daga Manzon Allah (saww) yana cewa:
“YA KU JAMA’AR MUSULMAI, INA GARGADINKU AKAN ZINA (KU NISANCETA). DOMIN ACIKINTA AKWAI ABUBUWA GUDA SHIDA :
GUDA UKU ADUNIYA, GIDA UKU KUMA A LAHIRA. AMMA WADANDA SUKE ANAN DUNIYA SUNE :
1. Gushewar Kwarjini.
2. Dawwamammen Talauci.
3. Gajartar rayuwa (Wato rayuwarsu ba zatayi tsawo ba).
AMMA WADANDA ZASU RISKA A LAHIRA SUNE :
1. Fushin Allah.
2. Mummunan Hisabi.
3. Dawwama acikin Wuta.
A duba littafi mai suna “Akhbarun Nisa’, babin dake magana akan haramcin zina.
Shin dama mazinaci idan ya mutu yana zina, ashe zai dawwama acikin wuta,?kamar yadda wannan hadisin yayi bayani.
Wassalmu alaikum warahatullah wabarkatahu.